Duk surori

Surah 80

He Frowned

سُورَةُ عَبَسَ

Abasa · Makkan

Maɓalli: J na gaba aya · K ayah ta gaba

Audio
  1. 1

    بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ عَبَسَ وَتَوَلَّىٰٓ

    Tafsiri: 'Abasa wa tawallaa.

    Yã game huska kuma ya jũya bãya.

  2. 2

    أَن جَآءَهُ ٱلْأَعْمَىٰ

    Tafsiri: An jaa-ahul 'a-maa

    Sabõda makãho yã je masa.

  3. 3

    وَمَا يُدْرِيكَ لَعَلَّهُۥ يَزَّكَّىٰٓ

    Tafsiri: Wa maa yudreeka la'allahu yaz zakkaa.

    To, me ya sanar da kai cẽwa watakila shi ne zai tsarkaka.

  4. 4

    أَوْ يَذَّكَّرُ فَتَنفَعَهُ ٱلذِّكْرَىٰٓ

    Tafsiri: Au yaz zak karu fatanfa 'ahuz zikraa.

    Ko ya tuna, dõmin tunãwar ta amfane shi?

  5. 5

    أَمَّا مَنِ ٱسْتَغْنَىٰ

    Tafsiri: Amma manis taghnaa

    Amma wanda ya wadãtu da dũkiya.

  6. 6

    فَأَنتَ لَهُۥ تَصَدَّىٰ

    Tafsiri: Fa-anta lahu tasaddaa

    Sa'an nan kai kuma ka ɗora bijira zuwa gare shi!

  7. 7

    وَمَا عَلَيْكَ أَلَّا يَزَّكَّىٰ

    Tafsiri: Wa ma 'alaika allaa yaz zakka.

    To, me zai cũce ka idan bai tsarkaka ba?

  8. 8

    وَأَمَّا مَن جَآءَكَ يَسْعَىٰ

    Tafsiri: Wa amma man jaa-aka yas'a

    Kuma, amma wanda ya zomaka yana gaugãwa.

  9. 9

    وَهُوَ يَخْشَىٰ

    Tafsiri: Wahuwa yakhshaa,

    Alhãli shĩ yanã jin tsõrõn Allah.

  10. 10

    فَأَنتَ عَنْهُ تَلَهَّىٰ

    Tafsiri: Fa-anta 'anhu talah haa.

    Kai kuma kã shagala ga barinsa!

  11. 11

    كَلَّآ إِنَّهَا تَذْكِرَةٌۭ

    Tafsiri: Kalla innaha tazkirah

    A'aha! Lalle ne, wannan tunãtarwa ce.

  12. 12

    فَمَن شَآءَ ذَكَرَهُۥ

    Tafsiri: Faman shaa a zakarah

    Sabõda wanda ya so ya tunaShi (Allah).

  13. 13

    فِى صُحُفٍۢ مُّكَرَّمَةٍۢ

    Tafsiri: Fi suhufim mukar rama,

    (Tunãtarwa ce) ta cikin littafai abãban girmamãwa,

  14. 14

    مَّرْفُوعَةٍۢ مُّطَهَّرَةٍۭ

    Tafsiri: Marfoo'atim mutah hara,

    Abãban ɗaukakãwa, abãban tsarkakẽwa.

  15. 15

    بِأَيْدِى سَفَرَةٍۢ

    Tafsiri: Bi'aidee safara

    A cikin hannãyen mala'iku marubũta.

  16. 16

    كِرَامٍۭ بَرَرَةٍۢ

    Tafsiri: Kiraamim bararah.

    Mãsu daraja, mãsu ɗã'a ga Allah.

  17. 17

    قُتِلَ ٱلْإِنسَٰنُ مَآ أَكْفَرَهُۥ

    Tafsiri: Qutilal-insanu maa akfarah.

    An la'ani mutum (kafiri). Mẽ yã yi kãfircinsa!

  18. 18

    مِنْ أَىِّ شَىْءٍ خَلَقَهُۥ

    Tafsiri: Min aiyyi shai-in Khalaq

    Daga wane abu, (Allah) Ya halitta shi?

  19. 19

    مِن نُّطْفَةٍ خَلَقَهُۥ فَقَدَّرَهُۥ

    Tafsiri: Min nutfah; khalaqahu faqad-darah.

    Daga ɗigon maniyyi, Ya halitta shi sa'an nan Ya ƙaddarã shi (ga halaye).

  20. 20

    ثُمَّ ٱلسَّبِيلَ يَسَّرَهُۥ

    Tafsiri: Thummas sabeela yas-sarah

    Sa'an nan, hanyarsa ta fita Ya sauƙaƙe masa.

  21. 21

    ثُمَّ أَمَاتَهُۥ فَأَقْبَرَهُۥ

    Tafsiri: Thumma amatahu fa-aqbarah

    Sa'an nan, Ya matar da shi sai Ya sanya shi a cikin kabari.

  22. 22

    ثُمَّ إِذَا شَآءَ أَنشَرَهُۥ

    Tafsiri: Thumma iza shaa-a ansharah

    Sa'an nan, idan Ya so lalle ne zai tãyar da shi.

  23. 23

    كَلَّا لَمَّا يَقْضِ مَآ أَمَرَهُۥ

    Tafsiri: Kalla lamma yaqdi maa amarah.

    Haƙĩƙa bai i da aikata abin da Allah Ya umurce shi ba (lõkacin sanya shi a cikin kabari).

  24. 24

    فَلْيَنظُرِ ٱلْإِنسَٰنُ إِلَىٰ طَعَامِهِۦٓ

    Tafsiri: Falyanzuril insanu ilaa ta-amih

    To, mutum ya dũba zuwa ga abincinsa.

  25. 25

    أَنَّا صَبَبْنَا ٱلْمَآءَ صَبًّۭا

    Tafsiri: Anna sabab nalmaa-a sabba.

    Lalle ne Mũ, Mun zuo ruwa, zubõwa.

  26. 26

    ثُمَّ شَقَقْنَا ٱلْأَرْضَ شَقًّۭا

    Tafsiri: Thumma sha qaqnal-arda shaqqa.

    Sa'an nan, Muka tsattsãge ƙasa tsattsagewa.

  27. 27

    فَأَنۢبَتْنَا فِيهَا حَبًّۭا

    Tafsiri: Fa ambatna feeha habba

    Sa'an nan, Muka tsirar da ƙwaya, a cikinta.

  28. 28

    وَعِنَبًۭا وَقَضْبًۭا

    Tafsiri: Wa 'inabaw-wa qadba

    Da inabi da ciyãwa.

  29. 29

    وَزَيْتُونًۭا وَنَخْلًۭا

    Tafsiri: Wa zaitoonaw wanakh la'

    Da zaitũni da itãcen dabĩno.

  30. 30

    وَحَدَآئِقَ غُلْبًۭا

    Tafsiri: Wa hadaa-iqa ghulba

    Da lambuna, mãsu yawan itãce.

  31. 31

    وَفَٰكِهَةًۭ وَأَبًّۭا

    Tafsiri: Wa faki hataw-wa abba.

    Da 'yã'yan itãcen marmari, da makiyãyã ta dabbõbi.

  32. 32

    مَّتَٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ

    Tafsiri: Mata'al-lakum wa li-an'amikum.

    Domin jin dãɗi a gare ku, ku da dabbobinku.

  33. 33

    فَإِذَا جَآءَتِ ٱلصَّآخَّةُ

    Tafsiri: Faiza jaa-atis saakhah.

    To, idan mai tsãwa (busa ta biyu) ta zo.

  34. 34

    يَوْمَ يَفِرُّ ٱلْمَرْءُ مِنْ أَخِيهِ

    Tafsiri: Yauma yafir-rul mar-u min akheeh

    Rãnar da mutum yake gudu daga ɗan'uwansa.

  35. 35

    وَأُمِّهِۦ وَأَبِيهِ

    Tafsiri: Wa ummihee wa abeeh

    Da uwarsa da ubansa.

  36. 36

    وَصَٰحِبَتِهِۦ وَبَنِيهِ

    Tafsiri: Wa sahi batihee wa baneeh.

    Da mãtarsa da ɗiyansa.

  37. 37

    لِكُلِّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ يَوْمَئِذٍۢ شَأْنٌۭ يُغْنِيهِ

    Tafsiri: Likul limri-im-minuhm yaumaa-izin shaa nuy-yughneeh

    Ga kõwane mutum daga cikinsu, a rãnar nan akwai wani sha'ani da ya ishe shi.

  38. 38

    وُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍۢ مُّسْفِرَةٌۭ

    Tafsiri: Wujoo huny-yauma-izim-musfira;

    Wasu huskõki, a rãnar nan, mãsu haske ne.

  39. 39

    ضَاحِكَةٌۭ مُّسْتَبْشِرَةٌۭ

    Tafsiri: Dahi katum mustab shirah

    Mãsu dãriya ne, mãsu bushãra.

  40. 40

    وَوُجُوهٌۭ يَوْمَئِذٍ عَلَيْهَا غَبَرَةٌۭ

    Tafsiri: Wa wujoohuy yauma-izin 'alaiha ghabar a

    Wasu huskõki, a rãnar nan, akwai ƙũra a kansu.

  41. 41

    تَرْهَقُهَا قَتَرَةٌ

    Tafsiri: Tarhaquha qatarah.

    Baƙi zai rufe su.

  42. 42

    أُو۟لَٰٓئِكَ هُمُ ٱلْكَفَرَةُ ٱلْفَجَرَةُ

    Tafsiri: Ulaa-ika humul-kafa ratul-fajarah.

    Waɗannan sũ ne kãfirai fãjirai (ga ayyukansu).

Buga fassarar: _IWPH_0__

Verse audio: Mishary Rashid Alafasy (128kbps via islamic.network CDN).

Rubutu da fassarorinsu: api.alquran.cloud · Uthmani Larabci.

Idan ma'anar ayah ba ta da tabbas, tambayi ƙwararren malami - musamman don batutuwan shari'a da ƙa'ida.