Duk surori

Surah 79

Those who drag forth

سُورَةُ النَّازِعَاتِ

An-Naazi'aat · Makkan

Maɓalli: J na gaba aya · K ayah ta gaba

Audio
  1. 1

    بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ وَٱلنَّٰزِعَٰتِ غَرْقًۭا

    Tafsiri: Wan naazi 'aati gharqa

    Ina rantsuwa da mala'iku mãsu fisgar rãyuka (na kafirai) da ƙarfi.

  2. 2

    وَٱلنَّٰشِطَٰتِ نَشْطًۭا

    Tafsiri: Wan naa shi taati nashta

    Da mãsu ɗibar rãyuka (na mũminai) da sauƙi a cikin nishãɗi.

  3. 3

    وَٱلسَّٰبِحَٰتِ سَبْحًۭا

    Tafsiri: Wass saabi-haati sabha

    Da mãsu sauka daga sama da umurnin Allah kamar suna iyo.

  4. 4

    فَٱلسَّٰبِقَٰتِ سَبْقًۭا

    Tafsiri: Fass saabi qaati sabqa

    Sa'an nan, su zama mãsu gaugãwa (da umurnin Allah) kamar suna tsẽre.

  5. 5

    فَٱلْمُدَبِّرَٰتِ أَمْرًۭا

    Tafsiri: Fal mu dab-bi raati amra

    Sa, an nan, su kasance masu shirya gudanar da umurni.

  6. 6

    يَوْمَ تَرْجُفُ ٱلرَّاجِفَةُ

    Tafsiri: Yawma tarjufur raajifa

    Rãnar da mai girgiza abũbuwa (bũsar farko) zã ta kaɗa.

  7. 7

    تَتْبَعُهَا ٱلرَّادِفَةُ

    Tafsiri: Tatba'u har raadifa

    Mai biyar ta (bũsa ta biyu) nã biye.

  8. 8

    قُلُوبٌۭ يَوْمَئِذٍۢ وَاجِفَةٌ

    Tafsiri: Quloobuny-yau maaiziw-waaji-fa

    Wasu zukãta, a rãnar nan, mãsu jin tsõro ne.

  9. 9

    أَبْصَٰرُهَا خَٰشِعَةٌۭ

    Tafsiri: Absaa ruhaa khashi'ah

    Alhãli idãnunsu na ƙasƙantattu.

  10. 10

    يَقُولُونَ أَءِنَّا لَمَرْدُودُونَ فِى ٱلْحَافِرَةِ

    Tafsiri: Ya qoo loona a-inna lamar doo doona fil haafirah

    Sunã cẽwa "Ashe lalle zã a iya mayar da mu a kan sãwunmu?

  11. 11

    أَءِذَا كُنَّا عِظَٰمًۭا نَّخِرَةًۭ

    Tafsiri: Aizaa kunna 'izaa man-nakhirah

    "Ashe, idan muka zama ƙasusuwa rududdugaggu?"

  12. 12

    قَالُوا۟ تِلْكَ إِذًۭا كَرَّةٌ خَاسِرَةٌۭ

    Tafsiri: Qaalu tilka izan karratun khaasirah.

    Suka ce: "Waccan kam kõmãwa ce, tãɓaɓɓiya!"

  13. 13

    فَإِنَّمَا هِىَ زَجْرَةٌۭ وَٰحِدَةٌۭ

    Tafsiri: Fa inna ma hiya zajratuw-waahida

    To, ita kam, tsãwa guda kawai ce.

  14. 14

    فَإِذَا هُم بِٱلسَّاهِرَةِ

    Tafsiri: Faizaa hum biss saahirah

    Sai kawai gã su a bãyan ƙasa.

  15. 15

    هَلْ أَتَىٰكَ حَدِيثُ مُوسَىٰٓ

    Tafsiri: Hal ataaka hadeethu Musaa

    Shin, lãbãrin Mũsã ya zo maka?

  16. 16

    إِذْ نَادَىٰهُ رَبُّهُۥ بِٱلْوَادِ ٱلْمُقَدَّسِ طُوًى

    Tafsiri: Iz nadaahu rabbuhu bil waadil-muqad dasi tuwa

    A lõkacin da Ubangijinsa Ya kirãye shi, a cikin kwari mai tsarki, wato Duwã?

  17. 17

    ٱذْهَبْ إِلَىٰ فِرْعَوْنَ إِنَّهُۥ طَغَىٰ

    Tafsiri: Izhab ilaa fir'auna innahu taghaa.

    Ka tafi zuwa ga Fir'auna, lalle ne shi, ya ƙẽtare haddi.

  18. 18

    فَقُلْ هَل لَّكَ إِلَىٰٓ أَن تَزَكَّىٰ

    Tafsiri: Faqul hal laka ilaa-an tazakka.

    "Sai ka ce masa, Kõ zã ka so ka tsarkaka.

  19. 19

    وَأَهْدِيَكَ إِلَىٰ رَبِّكَ فَتَخْشَىٰ

    Tafsiri: Wa ahdi yaka ila rabbika fatakh sha

    "Kuma in shiryar da kai zuwa ga Ubangijinka domin ka ji tsoronSa?"

  20. 20

    فَأَرَىٰهُ ٱلْءَايَةَ ٱلْكُبْرَىٰ

    Tafsiri: Fa araahul-aayatal kubra.

    Sai ya nũna masa ãyar nan mafi girma.

  21. 21

    فَكَذَّبَ وَعَصَىٰ

    Tafsiri: Fa kazzaba wa asaa.

    Sai ya ƙaryata, kuma ya sãɓa (umurni),

  22. 22

    ثُمَّ أَدْبَرَ يَسْعَىٰ

    Tafsiri: Thumma adbara yas'aa.

    Sa'an nan ya jũya bãya, yanã tafiya da sauri.

  23. 23

    فَحَشَرَ فَنَادَىٰ

    Tafsiri: Fa hashara fanada.

    Sai ya yi gayya, sa'an nan ya yi kira.

  24. 24

    فَقَالَ أَنَا۠ رَبُّكُمُ ٱلْأَعْلَىٰ

    Tafsiri: Faqala ana rabbu kumul-a'laa.

    Sai ya ce: "Nĩ ne Ubangijinku mafi ɗaudaka."

  25. 25

    فَأَخَذَهُ ٱللَّهُ نَكَالَ ٱلْءَاخِرَةِ وَٱلْأُولَىٰٓ

    Tafsiri: Fa-akha zahul laahu nakalal aakhirati wal-oola.

    Sabõda haka Allah Ya kama shi, dõmin azãbar maganar ƙarshe da ta farko.

  26. 26

    إِنَّ فِى ذَٰلِكَ لَعِبْرَةًۭ لِّمَن يَخْشَىٰٓ

    Tafsiri: Inna fee zaalika la'ibratal limaiy-yaksha

    Lalle ne, a cikin wannan haƙiƙa akwai abin kula ga wanda yake tsõron Allah.

  27. 27

    ءَأَنتُمْ أَشَدُّ خَلْقًا أَمِ ٱلسَّمَآءُ ۚ بَنَىٰهَا

    Tafsiri: A-antum a shaddu khalqan amis samaa-u banaaha.

    Shin, kũ ne mafi wuyar halitta ko sama? Allah Ya gina ta.

  28. 28

    رَفَعَ سَمْكَهَا فَسَوَّىٰهَا

    Tafsiri: Raf'a sam kaha fasaw waaha

    Ya ɗaukaka rufinta, sa'an nan Ya daidaita ta.

  29. 29

    وَأَغْطَشَ لَيْلَهَا وَأَخْرَجَ ضُحَىٰهَا

    Tafsiri: Wa aghtasha lailaha wa akhraja duhaaha.

    Kuma Ya duhuntar da darenta, kuma Ya fitar da hantsinta.

  30. 30

    وَٱلْأَرْضَ بَعْدَ ذَٰلِكَ دَحَىٰهَآ

    Tafsiri: Wal arda b'ada zaalika dahaaha.

    Kuma, ƙasa a bayan haka Ya mulmula ta.

  31. 31

    أَخْرَجَ مِنْهَا مَآءَهَا وَمَرْعَىٰهَا

    Tafsiri: Akhraja minha maa-aha wa mar 'aaha.

    Ya fitar da ruwanta daga gare ta da makiyãyarta.

  32. 32

    وَٱلْجِبَالَ أَرْسَىٰهَا

    Tafsiri: Wal jibala arsaaha.

    Da duwatsu, Yã kafe ta.

  33. 33

    مَتَٰعًۭا لَّكُمْ وَلِأَنْعَٰمِكُمْ

    Tafsiri: Mataa'al lakum wali an 'aamikum.

    Domin jiyarwa dãɗi a gare ku, kuma ga dabbõbinku.

  34. 34

    فَإِذَا جَآءَتِ ٱلطَّآمَّةُ ٱلْكُبْرَىٰ

    Tafsiri: Fa-izaa jaaa'atit taaam matul kubraa.

    To, idan uwar masĩfu, mafi girma, ta zo.

  35. 35

    يَوْمَ يَتَذَكَّرُ ٱلْإِنسَٰنُ مَا سَعَىٰ

    Tafsiri: Yauma Yata zakkarul insaanu ma sa'aa.

    Rãnar da mutum zai yi tunãnin abin da ya aikata.

  36. 36

    وَبُرِّزَتِ ٱلْجَحِيمُ لِمَن يَرَىٰ

    Tafsiri: Wa burrizatil-jaheemu limany-yaraa.

    Kuma, a bayyana Jahĩm ga mai gani.

  37. 37

    فَأَمَّا مَن طَغَىٰ

    Tafsiri: Fa ammaa man taghaa.

    To, amma wanda ya yi girman kai.

  38. 38

    وَءَاثَرَ ٱلْحَيَوٰةَ ٱلدُّنْيَا

    Tafsiri: Wa aasaral hayaatad dunyaa

    Kuma, ya zãɓi rãyuwa ta kusa, (wato dũniya).

  39. 39

    فَإِنَّ ٱلْجَحِيمَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ

    Tafsiri: Fa innal jaheema hiyal maawaa.

    To, lalle ne Jahĩm, ita ce makõma.

  40. 40

    وَأَمَّا مَنْ خَافَ مَقَامَ رَبِّهِۦ وَنَهَى ٱلنَّفْسَ عَنِ ٱلْهَوَىٰ

    Tafsiri: Wa ammaa man khaafa maqaama Rabbihee wa nahan nafsa 'anil hawaa

    Kuma, amma wanda ya ji tsõron tsayi a gaba ga Ubangijinsa, kuma ya kange kansa daga son rai.

  41. 41

    فَإِنَّ ٱلْجَنَّةَ هِىَ ٱلْمَأْوَىٰ

    Tafsiri: Fa innal jannata hiyal maawaa

    To, lalle ne Aljanna ita ce makõma.

  42. 42

    يَسْـَٔلُونَكَ عَنِ ٱلسَّاعَةِ أَيَّانَ مُرْسَىٰهَا

    Tafsiri: Yas'aloonaka 'anis saa'ati ayyaana mursaahaa

    Sunã tambayar ka game da sa'a, wai yaushe ne matabbatarta?

  43. 43

    فِيمَ أَنتَ مِن ذِكْرَىٰهَآ

    Tafsiri: Feema anta min zikraahaa

    Me ya haɗã ka da ambatonta?

  44. 44

    إِلَىٰ رَبِّكَ مُنتَهَىٰهَآ

    Tafsiri: Ilaa Rabbika muntahaa haa

    Zuwa ga Ubangijinka ƙarshen al'amarinta yake.

  45. 45

    إِنَّمَآ أَنتَ مُنذِرُ مَن يَخْشَىٰهَا

    Tafsiri: Innamaaa anta munziru maiy yakshaahaa

    Kai mai gargaɗi kawai ne ga mai tsõron ta.

  46. 46

    كَأَنَّهُمْ يَوْمَ يَرَوْنَهَا لَمْ يَلْبَثُوٓا۟ إِلَّا عَشِيَّةً أَوْ ضُحَىٰهَا

    Tafsiri: Ka annahum Yawma yarawnahaa lam yalbasooo illaa 'ashiyyatan aw duhaahaa

    Kamar sũ a rãnar da zã su gan ta, ba su zauna ba fãce a lõkacin marẽce ko hantsinsa.

Buga fassarar: _IWPH_0__

Verse audio: Mishary Rashid Alafasy (128kbps via islamic.network CDN).

Rubutu da fassarorinsu: api.alquran.cloud · Uthmani Larabci.

Idan ma'anar ayah ba ta da tabbas, tambayi ƙwararren malami - musamman don batutuwan shari'a da ƙa'ida.