Duk surori

Surah 78

The Tidings

سُورَةُ النَّبَإِ

An-Naba · Makkan

Maɓalli: J na gaba aya · K ayah ta gaba

Audio
  1. 1

    بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ عَمَّ يَتَسَآءَلُونَ

    Tafsiri: 'Amma Yatasaa-aloon

    A kan mẽ suke tambayar jũna?

  2. 2

    عَنِ ٱلنَّبَإِ ٱلْعَظِيمِ

    Tafsiri: 'Anin-nabaa-il 'azeem

    A kan muhimmin lãbãri mai girma (Alƙur'ãni)?

  3. 3

    ٱلَّذِى هُمْ فِيهِ مُخْتَلِفُونَ

    Tafsiri: Allazi hum feehi mukh talifoon

    Wanda suke sãɓa wa jũna a cikinsa?

  4. 4

    كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

    Tafsiri: Kallaa sa y'alamoon

    A'aha! Zã su sani.

  5. 5

    ثُمَّ كَلَّا سَيَعْلَمُونَ

    Tafsiri: Thumma kallaa sa y'alamoon

    Kuma, a'aha! Zã su sani.

  6. 6

    أَلَمْ نَجْعَلِ ٱلْأَرْضَ مِهَٰدًۭا

    Tafsiri: Alam naj'alil arda mihaa da

    Ashe, ba Mu sanya ƙasa shimfiɗa ba?

  7. 7

    وَٱلْجِبَالَ أَوْتَادًۭا

    Tafsiri: Wal jibaala au taada

    Da duwãtsu turaku (ga riƙe ƙasa)?

  8. 8

    وَخَلَقْنَٰكُمْ أَزْوَٰجًۭا

    Tafsiri: Wa khalaq naakum azwaaja

    Kuma, Mun halitta ku mazã da mãtã?

  9. 9

    وَجَعَلْنَا نَوْمَكُمْ سُبَاتًۭا

    Tafsiri: Waja'alnan naumakum subata

    Kuma, Muka sanya barcinku hũtãwa?

  10. 10

    وَجَعَلْنَا ٱلَّيْلَ لِبَاسًۭا

    Tafsiri: Waja'alnal laila libasa

    Kuma, Muka sanya dare (ya zama) sutura?

  11. 11

    وَجَعَلْنَا ٱلنَّهَارَ مَعَاشًۭا

    Tafsiri: Waja'alnan nahara ma 'aasha

    Kuma, Muka sanya yini (yazama) lõkacin nẽman abinci?

  12. 12

    وَبَنَيْنَا فَوْقَكُمْ سَبْعًۭا شِدَادًۭا

    Tafsiri: Wa banaina fauqakum sab 'an shi daada

    Kuma, Muka gina, a samanku, sammai bakwai mãsu ƙarfi?

  13. 13

    وَجَعَلْنَا سِرَاجًۭا وَهَّاجًۭا

    Tafsiri: Waja'alna siraajaw wah haaja

    Kuma, Muka sanya fitila mai tsanin haske (rãnã)?

  14. 14

    وَأَنزَلْنَا مِنَ ٱلْمُعْصِرَٰتِ مَآءًۭ ثَجَّاجًۭا

    Tafsiri: Wa anzalna minal m'usiraati maa-an saj-jaaja

    Kuma, Muka saukar daga cikakkun girãgizai, ruwa mai yawan zuba?

  15. 15

    لِّنُخْرِجَ بِهِۦ حَبًّۭا وَنَبَاتًۭا

    Tafsiri: Linukh rija bihee habbaw wana baata

    Dõmin, Mu fitar da ƙwaya da tsiri game da shi?

  16. 16

    وَجَنَّٰتٍ أَلْفَافًا

    Tafsiri: Wa jan naatin alfafa

    Da itãcen lambuna mãsu lillibniya?

  17. 17

    إِنَّ يَوْمَ ٱلْفَصْلِ كَانَ مِيقَٰتًۭا

    Tafsiri: Inna yaumal-fasli kana miqaata

    Lalle ne, rãnar rarrabẽwa tã kasance abin ƙayyadẽ wa lõkaci.

  18. 18

    يَوْمَ يُنفَخُ فِى ٱلصُّورِ فَتَأْتُونَ أَفْوَاجًۭا

    Tafsiri: Yauma yun fakhu fis-soori fataa toona afwaaja

    Rãnar da zã a yi bũsa a cikin ƙaho, sai ku zo, jama'a jama'a.

  19. 19

    وَفُتِحَتِ ٱلسَّمَآءُ فَكَانَتْ أَبْوَٰبًۭا

    Tafsiri: Wa futiha tis samaa-u fakaanat abwaaba

    Kuma, aka buɗe sama, sai ta kasance ƙõfõfi.

  20. 20

    وَسُيِّرَتِ ٱلْجِبَالُ فَكَانَتْ سَرَابًا

    Tafsiri: Wa suyyi raatil jibaalu fa kaanat saraaba

    Kuma, aka tafiyar da duwãtsu, sai suka kasance ƙũra.

  21. 21

    إِنَّ جَهَنَّمَ كَانَتْ مِرْصَادًۭا

    Tafsiri: Inna jahan nama kaanat mirsaada

    Lalle ne, Jahannama tã kasance madãkata.

  22. 22

    لِّلطَّٰغِينَ مَـَٔابًۭا

    Tafsiri: Lit taa gheena ma aaba

    Ga mãsu ƙẽtare iyãkõki, tã zama makõma.

  23. 23

    لَّٰبِثِينَ فِيهَآ أَحْقَابًۭا

    Tafsiri: Laa bitheena feehaa ahqaaba

    Sunã, mãsu zama a cikinta, zãmunna.

  24. 24

    لَّا يَذُوقُونَ فِيهَا بَرْدًۭا وَلَا شَرَابًا

    Tafsiri: Laa ya zooqoona feeha bar daw walaa sharaaba

    Bã su ɗanɗanãwar wani sanyi a cikinta, kuma bã su ɗanɗana abin sha.

  25. 25

    إِلَّا حَمِيمًۭا وَغَسَّاقًۭا

    Tafsiri: Illa hamee maw-wa ghas saaqa

    Fãce tafasasshen ruwa da ruɓaɓɓen jini.

  26. 26

    جَزَآءًۭ وِفَاقًا

    Tafsiri: Jazaa-aw wi faaqa

    Sakamako mai dãcẽwa.

  27. 27

    إِنَّهُمْ كَانُوا۟ لَا يَرْجُونَ حِسَابًۭا

    Tafsiri: Innahum kaanu laa yarjoona hisaaba

    Lalle ne, sũ, sun kasance bã su fãtar sauƙin wani hisãbi.

  28. 28

    وَكَذَّبُوا۟ بِـَٔايَٰتِنَا كِذَّابًۭا

    Tafsiri: Wa kazzabu bi aayaa tina kizzaba

    Kuma, suka ƙaryata game da ãyõyinMu, ƙaryatãwa!

  29. 29

    وَكُلَّ شَىْءٍ أَحْصَيْنَٰهُ كِتَٰبًۭا

    Tafsiri: Wa kulla shai-in ahsai naahu kitaa ba

    Alhãli, kõwane abu Mun ƙididdigẽ shi, a rubũce.

  30. 30

    فَذُوقُوا۟ فَلَن نَّزِيدَكُمْ إِلَّا عَذَابًا

    Tafsiri: Fa zooqoo falan-nazee dakum ill-laa azaaba

    Sabõda haka, ku ɗanɗana domin haka, bã zã Mu ƙara muku kõme ba fãce azãba.

  31. 31

    إِنَّ لِلْمُتَّقِينَ مَفَازًا

    Tafsiri: Inna lil mutta qeena mafaaza

    Lalle ne, mãsu taƙawã nã da wani wurin sãmun babban rabo.

  32. 32

    حَدَآئِقَ وَأَعْنَٰبًۭا

    Tafsiri: Hadaa-iqa wa a'anaa ba

    Lambuna da inabõbi.

  33. 33

    وَكَوَاعِبَ أَتْرَابًۭا

    Tafsiri: Wa kaawa 'iba at raaba

    Da cikakkun 'yammata, tsãrar jũna.

  34. 34

    وَكَأْسًۭا دِهَاقًۭا

    Tafsiri: Wa ka'san di haaqa

    Da hinjãlan giya cikakku.

  35. 35

    لَّا يَسْمَعُونَ فِيهَا لَغْوًۭا وَلَا كِذَّٰبًۭا

    Tafsiri: Laa yasma'oona fiha lagh waw walaa kizzaba

    Bã su jin yãsassar magana, a cikinta, kuma bã su jin ƙaryatãwa.

  36. 36

    جَزَآءًۭ مِّن رَّبِّكَ عَطَآءً حِسَابًۭا

    Tafsiri: Jazaa-am mir-rabbika ataa-an hisaaba

    Dõmin sakamako daga Ubangijinka, kyautã mai yawa.

  37. 37

    رَّبِّ ٱلسَّمَٰوَٰتِ وَٱلْأَرْضِ وَمَا بَيْنَهُمَا ٱلرَّحْمَٰنِ ۖ لَا يَمْلِكُونَ مِنْهُ خِطَابًۭا

    Tafsiri: Rabbis samaa waati wal ardi wa maa baina humar rahmaani laa yam likoona minhu khi taaba

    Ubangijin sammai da ƙasa da abin da yake a tsakãninsu, Mai rahama, bã su da ikon yin wata magana daga gare Shi.

  38. 38

    يَوْمَ يَقُومُ ٱلرُّوحُ وَٱلْمَلَٰٓئِكَةُ صَفًّۭا ۖ لَّا يَتَكَلَّمُونَ إِلَّا مَنْ أَذِنَ لَهُ ٱلرَّحْمَٰنُ وَقَالَ صَوَابًۭا

    Tafsiri: Yauma yaqoo mur roohu wal malaa-ikatu saf-fal laa yata kalla moona illa man azina lahur rahmaanu wa qaala sawaaba

    Rãnar da Rũhi da malã'iku zã su tsaya a cikin safu, bã su magana, sai wanda Allah Ya yi masa izni, kuma ya faɗi abin da ke daidai.

  39. 39

    ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلْحَقُّ ۖ فَمَن شَآءَ ٱتَّخَذَ إِلَىٰ رَبِّهِۦ مَـَٔابًا

    Tafsiri: Zaalikal yaumul haqqu faman shaa-at ta khaaza ill-laa rabbihi ma-aaba

    Wancan, shi ne yini na gaskiya; to wanda ya so, ya riƙa makõma zuwa ga Ubangijinsa.

  40. 40

    إِنَّآ أَنذَرْنَٰكُمْ عَذَابًۭا قَرِيبًۭا يَوْمَ يَنظُرُ ٱلْمَرْءُ مَا قَدَّمَتْ يَدَاهُ وَيَقُولُ ٱلْكَافِرُ يَٰلَيْتَنِى كُنتُ تُرَٰبًۢا

    Tafsiri: In naa anzar naakum azaaban qareebaiy-yauma yan zurul marr-u maa qaddamat yadaahu wa ya qoolul-kaafiru yaa lai tanee kuntu turaaba

    Lalle ne, Mũ, Mun yi muku gargaɗin azãba makusanciya, rãnar da mutum ke dũbi zuwa ga abin da hannãyensa suka aikata, kuma kafiri ya ce: "Kaitona, dã dai nã zama turɓãya!"

Buga fassarar: _IWPH_0__

Verse audio: Mishary Rashid Alafasy (128kbps via islamic.network CDN).

Rubutu da fassarorinsu: api.alquran.cloud · Uthmani Larabci.

Idan ma'anar ayah ba ta da tabbas, tambayi ƙwararren malami - musamman don batutuwan shari'a da ƙa'ida.