Duk surori

Surah 70

The Ascending Stairways

سُورَةُ المَعَارِجِ

Al-Ma'aarij · Makkan

Maɓalli: J na gaba aya · K ayah ta gaba

Audio
  1. 1

    بِسْمِ ٱللَّهِ ٱلرَّحْمَٰنِ ٱلرَّحِيمِ سَأَلَ سَآئِلٌۢ بِعَذَابٍۢ وَاقِعٍۢ

    Tafsiri: Sa ala saaa'ilum bi'azaa binw-waaqi'

    Wani mai tambaya yã yi tambaya game da azãba, mai aukuwa.

  2. 2

    لِّلْكَٰفِرِينَ لَيْسَ لَهُۥ دَافِعٌۭ

    Tafsiri: Lilkaafireen laisa lahoo daafi'

    Ga kãfirai, bã ta da mai tunkuɗẽwa.

  3. 3

    مِّنَ ٱللَّهِ ذِى ٱلْمَعَارِجِ

    Tafsiri: Minal laahi zil ma'aarij

    Daga Allah Mai matãkala.

  4. 4

    تَعْرُجُ ٱلْمَلَٰٓئِكَةُ وَٱلرُّوحُ إِلَيْهِ فِى يَوْمٍۢ كَانَ مِقْدَارُهُۥ خَمْسِينَ أَلْفَ سَنَةٍۢ

    Tafsiri: Ta'rujul malaaa'ikatu war Roohu ilaihi fee yawmin kaana miqdaaruhoo khamseena alfa sanah

    Malã'iku da Ruhi (Jibrila) sunã tãkãwa zuwa gare Shi, a cikin yini wanda gwargwadonsa, shẽkara dubu hamsin ne.

  5. 5

    فَٱصْبِرْ صَبْرًۭا جَمِيلًا

    Tafsiri: Fasbir ssabran jameelaa

    Sabõda haka, ka yi haƙuri, haƙuri mai kyãwo.

  6. 6

    إِنَّهُمْ يَرَوْنَهُۥ بَعِيدًۭا

    Tafsiri: Inaahum yarawnahoo ba'eedaa

    Lalle ne su, sunã ganin ta mai nĩsa.

  7. 7

    وَنَرَىٰهُ قَرِيبًۭا

    Tafsiri: Wa naraahu qareebaa

    Kuma Mu, Muna ganin ta a kusa.

  8. 8

    يَوْمَ تَكُونُ ٱلسَّمَآءُ كَٱلْمُهْلِ

    Tafsiri: Yawma takoonus samaaa'u kalmuhl

    Rãnar da sama zã ta kasance kamar narkakkar azurfa.

  9. 9

    وَتَكُونُ ٱلْجِبَالُ كَٱلْعِهْنِ

    Tafsiri: Wa takoonul jibaalu kal'ihn

    Kuma duwãtsu su zama kamar saɓin sũfi.

  10. 10

    وَلَا يَسْـَٔلُ حَمِيمٌ حَمِيمًۭا

    Tafsiri: Wa laa yas'alu hameemun hameemaa

    Kuma abõki bã ya tambayar inda wani abõki yake.

  11. 11

    يُبَصَّرُونَهُمْ ۚ يَوَدُّ ٱلْمُجْرِمُ لَوْ يَفْتَدِى مِنْ عَذَابِ يَوْمِئِذٍۭ بِبَنِيهِ

    Tafsiri: Yubassaroonahum; ya waddul mujrimu law yaftadee min 'azaabi yawma'izim bibaneeh

    Ana sanya su, su gajũna, mai laifi na gũrin dã zai iya yin fansa, daga azãbar rãnar nan, da ɗiyansa,

  12. 12

    وَصَٰحِبَتِهِۦ وَأَخِيهِ

    Tafsiri: Wa saahibatihee wa akheeh

    Da matarsa da ɗan'uwansa.

  13. 13

    وَفَصِيلَتِهِ ٱلَّتِى تُـْٔوِيهِ

    Tafsiri: Wa faseelathil latee tu'weeh

    Da danginsa, mãsu tattarã shi.

  14. 14

    وَمَن فِى ٱلْأَرْضِ جَمِيعًۭا ثُمَّ يُنجِيهِ

    Tafsiri: Wa man fil ardi jamee'an summa yunjeeh

    Da wanda ke a cikin dũniya duka gabã ɗaya, sa'an nan fansar, ta tsĩrar da shi.

  15. 15

    كَلَّآ ۖ إِنَّهَا لَظَىٰ

    Tafsiri: Kallaa innahaa lazaa

    A'aha! Lalle ne fa, ita ce Lazã,

  16. 16

    نَزَّاعَةًۭ لِّلشَّوَىٰ

    Tafsiri: Nazzaa'atal lishshawaa

    Mai twãle fãtar goshi.

  17. 17

    تَدْعُوا۟ مَنْ أَدْبَرَ وَتَوَلَّىٰ

    Tafsiri: Tad'oo man adbara wa tawallaa

    Tanã kiran wanda ya jũya bãya (daga addini) kuma ya kau da kai.

  18. 18

    وَجَمَعَ فَأَوْعَىٰٓ

    Tafsiri: W jama'a fa aw'aa

    Ya tãra (dũkiya), kuma ya sanya ta a cikin jaka.

  19. 19

    ۞ إِنَّ ٱلْإِنسَٰنَ خُلِقَ هَلُوعًا

    Tafsiri: Innal insaana khuliqa haloo'aa

    Lalle ne mutum an halitta shi mai ciwon kwaɗayi.

  20. 20

    إِذَا مَسَّهُ ٱلشَّرُّ جَزُوعًۭا

    Tafsiri: Izaa massahush sharru jazoo'aa

    Idan sharri ya shãfe shi, ya kãsa haƙuri.

  21. 21

    وَإِذَا مَسَّهُ ٱلْخَيْرُ مَنُوعًا

    Tafsiri: Wa izaa massahul khairu manoo'aa

    Kuma idan alhẽri ya shãfe shi, ya yi rõwa.

  22. 22

    إِلَّا ٱلْمُصَلِّينَ

    Tafsiri: Illal musalleen

    Sai mãsu yin salla,

  23. 23

    ٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ دَآئِمُونَ

    Tafsiri: Allazeena hum 'alaa Salaatihim daaa'imoon

    Waɗanda suke, a kan sallarsu, su, mãsu dawwama ne.

  24. 24

    وَٱلَّذِينَ فِىٓ أَمْوَٰلِهِمْ حَقٌّۭ مَّعْلُومٌۭ

    Tafsiri: Wallazeena feee amwaalihim haqqum ma'loom

    Kuma waɗanda a cikin dũkiyarsu, akwai wani haƙƙi sananne.

  25. 25

    لِّلسَّآئِلِ وَٱلْمَحْرُومِ

    Tafsiri: Lissaaa 'ili walmahroom

    Ga (matalauci) mai rõƙo da wanda aka hanã wa roƙon.

  26. 26

    وَٱلَّذِينَ يُصَدِّقُونَ بِيَوْمِ ٱلدِّينِ

    Tafsiri: Wallazeena yusaddiqoona bi yawmid Deen

    Da waɗannan da ke gaskata rãnar sakamako.

  27. 27

    وَٱلَّذِينَ هُم مِّنْ عَذَابِ رَبِّهِم مُّشْفِقُونَ

    Tafsiri: Wallazeena hum min 'azaabi Rabbihim mushfiqoon

    Da waɗannan sabõda azãbar Ubangijinsu, suna jin tsõro.

  28. 28

    إِنَّ عَذَابَ رَبِّهِمْ غَيْرُ مَأْمُونٍۢ

    Tafsiri: Inna 'azaaba Rabbihim ghairu maamoon

    Lalle ne, azãbar Ubangijinsu bã wadda ake iya amincẽwaba ce.

  29. 29

    وَٱلَّذِينَ هُمْ لِفُرُوجِهِمْ حَٰفِظُونَ

    Tafsiri: Wallazeena hum lifuroo jihim haafizoon

    Da waɗanda suke, ga farjojinsu, mãsu tsarewa ne.

  30. 30

    إِلَّا عَلَىٰٓ أَزْوَٰجِهِمْ أَوْ مَا مَلَكَتْ أَيْمَٰنُهُمْ فَإِنَّهُمْ غَيْرُ مَلُومِينَ

    Tafsiri: Illaa 'alaaa azwaajihim aw maa malakat aymaanuhum fainnahum ghairu maloomeen

    Sai fa a kan matan aurensu da abin da hannayensu na dãma suka mallaka. To lalle ne sũkam ba waɗanda ake zargi ba ne.

  31. 31

    فَمَنِ ٱبْتَغَىٰ وَرَآءَ ذَٰلِكَ فَأُو۟لَٰٓئِكَ هُمُ ٱلْعَادُونَ

    Tafsiri: Famanib taghaa waraaa'a zaalika fa ulaaa'ika humul 'aadoon

    To, duk wanda ya nẽmi abin da yake a bayan wannan, to, waɗancan sũ ne mãsu ƙetare iyãka.

  32. 32

    وَٱلَّذِينَ هُمْ لِأَمَٰنَٰتِهِمْ وَعَهْدِهِمْ رَٰعُونَ

    Tafsiri: Wallazeena hum li amaa naatihim wa 'ahdihim raa'oon

    Kuma da waɗannan da suke ga amãnõninsu da alkawarinsu mãsu tsarẽwa ne.

  33. 33

    وَٱلَّذِينَ هُم بِشَهَٰدَٰتِهِمْ قَآئِمُونَ

    Tafsiri: Wallazeena hum bishahaadaatihim qaaa'imoon

    Kuma da waɗanda suke, ga shaidarsu, mãsu dãgẽwa ne.

  34. 34

    وَٱلَّذِينَ هُمْ عَلَىٰ صَلَاتِهِمْ يُحَافِظُونَ

    Tafsiri: Wallazeena hum 'alaa salaatihim yuhaafizoon

    Kuma waɗanda suke, a kan sallarsu, mãsu tsarẽwa ne.

  35. 35

    أُو۟لَٰٓئِكَ فِى جَنَّٰتٍۢ مُّكْرَمُونَ

    Tafsiri: Ulaaa'ika fee jannaatim mukramoon

    Waɗannan, a cikin gidãjen Aljanna, waɗanda ake girmamãwa ne

  36. 36

    فَمَالِ ٱلَّذِينَ كَفَرُوا۟ قِبَلَكَ مُهْطِعِينَ

    Tafsiri: Famaa lil lazeena kafaroo qibalaka muhti'een

    Mẽ yã sãmi waɗanda suka kãfirta, a wajenka, sunã gaugãwar (gudu).

  37. 37

    عَنِ ٱلْيَمِينِ وَعَنِ ٱلشِّمَالِ عِزِينَ

    Tafsiri: 'Anil yameeni wa 'anish shimaali 'izeen

    Daga jihar dãma, kuma daga jihar hagu, jama'a-jama'a!

  38. 38

    أَيَطْمَعُ كُلُّ ٱمْرِئٍۢ مِّنْهُمْ أَن يُدْخَلَ جَنَّةَ نَعِيمٍۢ

    Tafsiri: Ayatma'u kullum ri'im minhum anyyudkhala jannata Na'eem

    Shin kõwane mutum daga cikinsu yana nẽman a shigar da shi a Aljannar ni'ima ne (ba da wani aiki ba)?

  39. 39

    كَلَّآ ۖ إِنَّا خَلَقْنَٰهُم مِّمَّا يَعْلَمُونَ

    Tafsiri: Kallaaa innaa khalaq nahum mimmaa ya'lamoon

    A'aha! Lalle Mũ, Mun halitta su, daga abin da suka sani.

  40. 40

    فَلَآ أُقْسِمُ بِرَبِّ ٱلْمَشَٰرِقِ وَٱلْمَغَٰرِبِ إِنَّا لَقَٰدِرُونَ

    Tafsiri: Falaaa uqsimu bi Rabbil mashaariqi wal maghaaribi innaa laqaadiroon

    Sabõda haka ba sai Na yi rantsuwa da Ubangijin wurãren ɓullõwar rãna da wurãren fãɗuwarta ba, lalle Mũ, Mãsu iyãwa ne.

  41. 41

    عَلَىٰٓ أَن نُّبَدِّلَ خَيْرًۭا مِّنْهُمْ وَمَا نَحْنُ بِمَسْبُوقِينَ

    Tafsiri: 'Alaaa an nubaddila khairam minhum wa maa Nahnu bimasbooqeen

    Ga Mu musanya waɗanda suke mafi alhẽri, daga gare su. Kuma ba Mu kasance waɗanda ake rinjãya ba.

  42. 42

    فَذَرْهُمْ يَخُوضُوا۟ وَيَلْعَبُوا۟ حَتَّىٰ يُلَٰقُوا۟ يَوْمَهُمُ ٱلَّذِى يُوعَدُونَ

    Tafsiri: Fazarhum yakhoodoo wa yal'aboo hattaa yulaaqoo yaw mahumul lazee yoo'adoon

    Sabõda haka ka bar su, su dulmuya, kuma su yi wãsã, har su haɗu da rãnarsu wadda ake yi musu alkawari (da ita).

  43. 43

    يَوْمَ يَخْرُجُونَ مِنَ ٱلْأَجْدَاثِ سِرَاعًۭا كَأَنَّهُمْ إِلَىٰ نُصُبٍۢ يُوفِضُونَ

    Tafsiri: Yawma yakhrujoona minal ajdaasi siraa'an ka anna hum ilaa nusubiny yoofidoon

    Rãnar da suke fitowa daga kaburbura da gaugãwa, kamar sũ, zuwa ga wata kafaffiyar (tuta), suke yin gaugãwa.

  44. 44

    خَٰشِعَةً أَبْصَٰرُهُمْ تَرْهَقُهُمْ ذِلَّةٌۭ ۚ ذَٰلِكَ ٱلْيَوْمُ ٱلَّذِى كَانُوا۟ يُوعَدُونَ

    Tafsiri: Khaashi'atan absaaruhum tarhaquhum zillah; zaalikal yawmul lazee kaanoo yoo'adoon

    Maƙaskanta ga idanunsu, wani walakanci yana rufe su. wannan shi ne yinin da suka kasance ana yi musa alkawari (a kansa.)

Buga fassarar: _IWPH_0__

Verse audio: Mishary Rashid Alafasy (128kbps via islamic.network CDN).

Rubutu da fassarorinsu: api.alquran.cloud · Uthmani Larabci.

Idan ma'anar ayah ba ta da tabbas, tambayi ƙwararren malami - musamman don batutuwan shari'a da ƙa'ida.

The Ascending Stairways — Islam Word